Labarai

Zargin Rashawa Na Neman Cin Wasu Kwamishinonin Hukumar ICPC

Zargin Rashawa Na Neman Cin Wasu Kwamishinonin Hukumar ICPC

Gwamnatin tarayya ta cire sunayen Maimuna Aliyu da Sa’ad Alanamu daga cikin jerin kwamishinonin hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC wadanda aka rantsar a makon da ya gabata bisa zargin rashawa da aka gabatar a kansu.

 

Kakakin Mukaddashin Shugaban Kasa, Akande Laolu ya ce za a binciki zargin da ake yi wa kwamishinonin biyu na almundahanar kudade na kusan Naira Bilyan daya inda ya nuna cewa binciken farko ya tabbatar da cewa babu wata kotu da ta taba tuhumarsu.