Yadda yan barandan siyasa suka afkawa yan majalisar dokokin jihar Kogi suna tsakiyar zama a zauren majalisa
Gungun matasa da ake zargin yan barandan siyasa ne sun kusta zauren majalisar dokokin jihar Kogi a inda suka yiwa yan majalisa duka kan mai uwa da wabi.
Wannan hoton daya daga cikin yan majalisar ne mai wakiltar mazabar Igalamela/Odulo, Hon. Friday Sani Makama wanda matasan suka tubewa kaya suka yiwa masa dukan mutuwa.
Hausa times ta ruiwato matasan kusan su 100 suka kutsa cikin majalisar duk da jami’an tsaro dake wajen a inda suka dirar wa yan majalisar suna tsakiyar zama a ranar Talata.
Dama ana takun saka tsakanin yan majalisar da Gwamnan jihar wanda hakan tasa ake zargin turo matasan akayi a cewar PoliticNgr
Me zaku CE?
Add Comment