Labarai

Tsagerun Naija Delta Sun Sha Alwashin Hana Hako Mai

Tsageru Neja-Delta Sun sha Alwashin Hana hako mai

Murna za ta koma ciki idan aka yi sake a Najeriya don kuwa Tsagerun Neja-Delta za su koma fasa bututun mai kamar yadda su ka fada.

A yanzu haka dai Najeriya na hako sama da ganga Miliyan 2 na danyen mai a kowace rana.

 

Ana ma sa rai hakan ya karu kamar yadda Ministan kasafin kudi Udo Udoma ya bayyana kwanan nan a wani taro da aka yi a Legas.

Wasu tsageru da ke Yankin Neja-Delta sun aikawa Dattijon Yankin Edwin Clark takarda cewa za su koma fasa bututun man kasar har sai ta kai ba a iya hako komai a Najeriya.

Wannan dai zai zama babbar matsala ga tattalin kasar idan aka yi sake.

Alkaluman kasar kamar yadda muka samu daga Fadar Shugaban kasa sun tabbatar da cewa tattalin arzikin kasar ya kama hanyar mikewa sarai.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.