Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ya yi amannar cewar Barack Obama ne ya kitsa jerin zanga-zangar kin ‘yan majalisar dokokin kasar na jam’iyyar Republikan da kuma fitar da wasu bayanan tsaron kasar.
Trump ya shaida gidan talabijin na Fox News cewar, “ina tunanin shugaba Obama ne ya kitsa lamarin saboda tabbas mutanensa ne suka hada abin. Na kuma yi tunanin cewar siyasa ce kawai.”
Mista Trump bai bayar da wata hujjar ikirarinsa ba, kuma magabacinsa a fadar White House, Barack Obama, bai yi tsokaci kan batun ba tukunna.
Add Comment