Labarai

Shin Kasan Mene Gaskia Game Da Lafiyar Shugaba Buhari

 

– Shugaban kungiyar daliban Najeriya (NANS), Chinonso Obasi ya bayyana cewa a hira da yayi da fadar shugaban kasa kwanan nan, Buhari zai dawo kan aikinsa nan ba da jimawa ba

– Shugaban kungiyar na NANS ya shawarci ‘yan Najeriya da su bi abunda ya dace a fafutukarsu kan lafiyar shugaban kasa

– A cewar Obasi, ya kamata a dauki rashin lafiyar Muhammadu Buhari a matsayin abun da zai zo ya wuce a kasar

Chinonso Obasi, shugaban kungiyar daliban Najeriya ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi ma shugaban kasa Muhammadu Buhari addu’a, a maimakon yi masa fatan mutuwa, NTA ta ruwaito.

Arewablog.com ta tattaro cewa a wata sanarwa wanda aka saki a Abuja, Obasi ya bayyana cewa bisa ga hira da yayi da fadar shugaban kasa a ranar 22 ga watan Yuli, Buhari zai dawo kwanan nan, kamar yadda yake samun lafiya sosai.

A cewar Obasi, bai kamata ba yadda aka mayar da lafiyar Buhari siyasa.

Obasi yaroki ya kamata a dauki rashin lafiyar Muhammadu Buhari a matsayin abun da zai zo ya wuce a kasar.