Wasanni

Salah Yana Son Karin Albashi A Liverpool

Rahotanni na cewa shahararren dan wasan kasar Masar, Mohammed Salah yana neman Liberpool ta amince za ta rika biyansa fam dubu dari biyar 500,000 duk mako
kafin ya sanya hannu a wani sabon kwantiragin ci gaba da yi mata wasa.

Kwaniragin dan wasan da Liverpool zai kare a shekarar 2023, kuma kungiyar ta zaku ta shiga sabuwar yarjejeniya da dan wasan a daidai lokacin da Real Madrid da Barcelona ke nemansa.

Amma wani sabon rahoto na cewa Salah na neman a rika biyansa rabin miliyan na kudin fam din Ingila duk mako domin ci gaba da zama Liverpool kuma kwanan nan Salah ya ce a shirye ya ke ya karkare kwantiraginsa da Liberpool, amma yana nema ya zama dan wasan da ya fi kowa daukar albashi a kungiyar.

A ranar Lahadin da ta gabata ya saka kwallo 3 rigis a ragar Manchester United, a wasan da Liverpool ta lallasa ta 5-0 a Old Trafford, sannan Salah ya kafa tarihin zama dan wasan Afrika da ya fi zura kwallo a gasar firimiyar Ingila a tarihi, inda a yanzu ya zarta Didier Drogba na Ivory Coast.

Yanzu haka Salah dan asalin kasar Masar ya jefa kwallaye 107 a gasar ta Firimiyar Ingila, yayin da a wasansu da Manchester United ya ci kwallaye uku shi kadai,. abin da a Turance ake cewa ‘Hat-trick’ sannan Salah ya sha gaban Drogba da ya buga wasa a Chelsea da kwallaye uku.

Sauran ‘yan wasan Afrika mafiya yawan kwallaye a gasar ta firiyar Ingila sun hada da Sadio Mane mai kwallaye 100, sai Emmanuel Adebayor mai kwallaye 97, yayin da Yakubu Ayegbemi ke da kwallaye 95.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.