Labarai

Ranar Alhamis Za A Yi Tsayuwar Arfa A Kasar Saudiyya

Daga Ibrahim Baba Suleiman

Gwamnatin Saudiyya ta bada shelar cewa ba’a ga jinjirin watan Dhul-Hijjah a ƙasar ranar Litinin ba kamar yadda ake tsamnanin sa a lissafin kalandar ƙasar, Saboda haka yau Talata zai zama 30 ga watan zul-qaada, Arafah zai zama ranar Alhamis 31 ga watan Agusta, kana ranar Juma’a ita ce ranar Sallar laiya a kasar Saudiyya.

 

Kazalika a Nijeriya yau Talata shine 29 ga watan Dhul-Qadah a lissafin ganin watan ƙasar, kuma yau ne Sarkin musulmin ƙasar, Muhammad Abubakar Sa’ad III ya bada shelar fara duba jinjirin wata a faɗin ƙasar, da fatan in an gani za’a sanar da mahukunta har ya kai ga Sarkin Musulmi.

Allah yasa mu dace.

 

“Souce In Rariya”

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.