Mujalla

Rahama Sadau Ta Shiga Cikin Mata Uku Masu Tashe A Arewa

Fitacciyar jarumar nan ta wasan kwaikwayon Hausa da turanci wato ta Kannywood da Nollywood Rahama Sadau ta shiga cikin jerin mata uku sa suka fi tashe a harkar fina-finai da nishadantarwa a yankin mu na arewacin Nigeria.

Jaridar Thisday ce dai ta wallafa sunaye gami da hotunan wadannan yan mata a shafinsu na instagram inda suka ayyana su a matsayin manya mata kuma masu tashe a bangaren nishadantarwa a arewa.

 

Wadannan shahararrun mata dai sune babbar mawakiyar nan Hadiza Blell wacce aka fi sani da suna Dija. Da kuma fitacciyar mai gabatar da shiri a gidan television wato Salma Phillips. Sai kuma jarumar wasan kwaikwayon Hausa Rahama Sadau.

 

About the author

Haarun

Co-founder Arewablog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.