Majalisar dattawan Najeriya ta amince da kudirin da zai bai wa matasa damar takarara mukaman shugaban kasa da gwamna da dan majalisar dattawa da na wakilai.
Kudirin dai ya bai wa matasa masu shekara 35 damar shiga takarar neman shugabancin kasar yayin da ya bai wa matasa masu shekara 30 damar neman gwamna.
Haka zalika, kudurin ya amince ‘yan shekara 25 su tsaya takarar zama wakilai a majalisar wakilan kasar.
‘Yan majalisar sun kuma amince da dan takara mai zaman kansa.
A ranar Talata ne dai matasa suka gangami a kan titunan Abuja babban birnin kasar domin yin tur da yunkurin watsi da kudurin kuma suka yi ta tafka muhara a shafukan sada zumunta kan maudu’in #NotTooYoungToRun.
A zamansu na ranar Laraba, ‘yan majalisar dattawan Najeriya sun kada kuri’u kan wasu kudurori na yi wa kundin tsarin mulkin kasar garambawul.
86 daga cikin ‘yan majalisar sun amince da kudurin yayin da 10 daga cikin suka ki amince da shi kuma dan majalisa daya ya ki kada kuri’a.
Souce In Bbchausa Abuja
Add Comment