Labarai

Nigeria: Kotu ta daure mawakin Hausa Sadiq Zazzabi

Sadiq Zazzabi mawaki ne da ke goyon bayan tsohon gwamnan Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso

Wata kotu a jihar Kanon Najeriya ta tura fitaccen mawakin Hausa Sadiq Zazzabi gidan kaso saboda wata sabuwar waka da ya fitar.
Shugaban hukumar ba da izinin wallafa fina-finai da wakoki ta jihar Kano, Ismaila Afakallahu, ya tabbatar wa jaridar Premium Times cewar mawakin mai suna Sadiq Zazzabi zai yi zaman kaso zuwa ranar Juma’a.
Hukumar ta ce duk da cewar mawakin ya gabatar da wakar gareta domin a bashi izinin wallafawa, bai jira a bashi izinin ba kafin ya kaddamar da ita. 
Amma shi mawakin ya ce ana hakon shi ne saboda yana goyon bayan tsohon gwamnan jihar, Rabi’u Musa Kwankwaso.
An dade ana samun takun-saka tsakanin tsohon gwamnan da gwamna mai ci yanzu a jihar Kano. 

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.