Labarai

Nigeria: Boko Haram ta sace masu bincike na NNPC goma

Kamfanin mai na Najeriya ya ce wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun sace masu binciken mai goma da suke masa aiki a jihar Borno da ke arewa maso gabashin kasar.

 

NNPC ya ce masana kimiyyar, wadanda wasunsu suka fito daga Jami’ar Maiduguri, sun shafe sama da shekara guda suna bincike kan abin da ya bayyana da tarin albarkatun mai a yankin Tafkin Chadi.

An yi awangaba da mutanen ne bayan wani kwantan bauna da aka yi musu a kusa da kauyen Jibi.

Mai magana da yawun NNPC Ndu Ughamadu ya ce mutanen sun “hada da malaman jami’a da direbobi da sauran ma’aikata”.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito mai magana da yawun Jami’ar Maiduguri yana cewa suna jiran karin bayani kan lamarin daga jami’an tsaro.

Sai dai ya tabbatar da cewa ma’aikatansu da suka yi tafi aikin bincike tare da jam’ian tsaro ba su dawo ba ranar Talata kamar yadda aka tsara.

Rikicin Boko Haram ya kashe sama da mutum 30,000 a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Yayin da wasu fiye miliyan biyu suka tsere daga gidajensu.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.