Labarai

Nigeria: Arzikin Aliko Dangote 'ya ragu'

Aliko Dangote ya dade yana shiga cikin jerin attajiran dduniya da Forbes ke wallafawa

Hamshakin dan kasuwar nan na Najeriya Aliko Dangote ya yi kasa a jerin masu kudin duniya inda ya fado daga mataki na 51 zuwa 105, in ji mujallar Forbes.

 
Mujallar ta ce arzikin Dangote ya ragu daga dala biliyan 15.4 a shekarar 2016 zuwa biliyan 12.2 a bana.
Hakan dai ya faru ne, a cewar Forbes, saboda faduwar darajar kudin Najeriya.
Alhaji Dangote, wanda ya fi karfi a harkar siminti da sukari da filawa, ya ja hankalin duniya lokacin da ya ce yana son sayen kulob din Arsenal cikin shekara hudu masu zuwa.
A ranar Alhamis ne, Shugaban kamfanin Amazon Jeff Bezos ya maye gurbin Bill Gates na wani dan lokaci a matsayin mutumin da ya fi kowa arziki a duniya.
Sai dai ba a jima ba ya koma mataki na biyu, inda mutumin da ya kirkiro kamfanin Microsoft din ya koma kan matsayinsa.