Siyasa

Nasarar Zaben Gwamna A Edo Nasarar Kwankwasiyya Ce -Sanata Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya t as ya Gwamnan jihar Edo wanda ya lashe zaben a jiya wato Godwin Obaseki

Kwankwaso ya bayyana hakane jiya ta hannun mai magana da yawunsa a kafafen sada zumunta Saifullahi Hassan.

Kwankwaso yace ina mika sakon taya murna zuwa mai Girma zababben Gwamnan Jihar Edo karo na biyu, mai girma Gov Godwin Obaseki.

Sannan kuma ina taya mutanen Jihar Edo bisa zaben PDP da sukayi kuma suka kare kuri’arsu.

Kwankwaso yace sakon godiya zuwa reshen Kwankwasiyya na jihar Edo da kuma shuwagabanni da yan arewa mazauna Edo bisa kokarinsu a wannan zabe – inji Kwankwaso

Kwankwaso dai shine wanda ya jagoranci jam iyyar sa ta PDP a kanfen din sabon Gwamnan Obaseki A zaben da aka gudanar ranar asabar data gabata.

About the author

Haarun

Co-founder Arewablog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Advertisement