Daga Haruna Suleiman Utono
Inji Fulanin Da Aminu Balarabe Kagara Yayiwa Gwanjon Shanu, Bayan Kwashe Sheka Biyar Da Gwanjon Shanun Marayu Batare da anbiyasu Shanayensu ba,
Kwatsam Sai Muka Wayi gari Da labarin anmaida Tshohon Alkalin da Yayi Gwanjon Shanunmu aiki, Tunda farko gwamnatin Jahar Neja a Karkashin Mu’azu Babangida Aliyu Ta kori Aminu Balarabe Kagara daga Alkalanci Bayan ansameshi da Gwanjon Shanu da Tumakai feye da 400
Mai Magana da Yawun Fulanin Haruna Suleiman Utono Yace Muddin Gwamnati Batayi Wani abuba duk abinda Ya biyo Baya Gwamnati Laifin Gwamnati ne, Saboda Kwamishinan Ayyuka na Jahar Neja Ibrahim Balarabe Kagara Wanda Yake Kaniga Aminu Balarabe Kagara Shine Keson haddasa rikici a Jahar Sakamakon Rufa rufa da Yakeyiwa Yayansa akan Badakalar Shanaye da Tumakai fiyeda 400 da Yayi,
- Advertisement -
Haruna Utono Yace Wadanda Yake Wakilta Sun Tabbatar Masa da Daukar Matakin Gayya a garin Kagara akan hakanne Ya nemi Subashi Mako biyu idan gwamnati Ta kasa yin Wani Abu Shima Zai chire hannunsa duk Matakin da Sukaga Yakamata Su dauka.
Haruna Utono Yayi Kiraga Gwamnan Jahar Neja da yayi Gaggawan Shiga lamarin tun kafin akaiga Zubar da Jini,
Tunda Farko Majalisar Dokokin Jahar Neja Ta fara Tattauna Maganar amma Saboda Shigar da Kara Kotu da Makiyayan Sukayi Sai Majalisar ta nemi dasu Janye Karar da Suka shigar Dan Kada suyiwa Kotu Katsalandar Fulanin Basuyi Wata wata ba Suka amince tare da Janye karar, amma daga Baya ‘Yan Majalisar Sukaki cika alkawarin da Suka dauka Wanda hakanne Yaba Kwamishannan ayyuka na Jahar Ibrahim Balarabe Kagara damar dawo da Kanin Nasa aiki inji Makiyayan.
#Mikiya