Wasanni

Man City na daf da daukar Danilo

City za ta dauki dan wasa Danilo kafin nan da ranan Litini

Ana sa ran Manchester City za ta kammala sayen dan wasan Real Madrid, Danilo kan kudi fan miliyan 26.5 nan da zuwa ranar Litinin.

Kocin Real, Zinedine Zidane ya ce dan kwallon mai shekara 26 mai buga wa tawagar Brazil tamaula ya bar inda kungiyar ke yin atisaye a Amurka ya ta fi City domin a duba lafiyarsa.

Sai dai an fahimci cewar har yanzun ba a gwada lafiyar dan wasan ba, kuma bai saka hannu kan yarjejeniya ba.

Ana sa ran Manchester City za ta kammala sayen Danilo kafin karawar da za ta yi da Real Madrid a ranar Laraba a gasar International Champions Cup a Amurka.

 

Souce In Bbchausa

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.