Labarai

Magoya Bayan Kanu Zasu Ja Tashin Hankali A Kasar Nan – Inji Almustapha

Magoya bayan Kanu zasu ja tashin hankali a kasan nan – Almustapha

An daure ni a kurkuku na taswon shekara 15 bisa zalunci

-Ina ganin su araba Najeriya a matsayin yan kungiya mai zaman kanta

Tsohon Babban Jami’in Tsaro ga marigayi Shugaban kasa, Janar Sani Abacha, Manjo Hamza Al-Mustapha, ya ce,ya ziyarci jihohin sassan kasanan dan yin wa’azin zaman lafiya,.

 

Al-Mustapha ya yi wannan maganan ne a Lagos. Allah madaukaki ya samar mun yanci na, bayan daurin da wa’yanda basa son yan Najeriya su san gaskiya suka mun har na tsawon shekaru 15 a kurkuku bisa zalunci

Ina ganin Dr. Frederick Fasehun a matsayin uba, mai jagoranci kuma mutumi mai girma. Na yaba da ruhin da ya kawo mu tare dashi da Comrade Oghenevo dan aikin samar da zama lafiya a Najeriya. Abun yabawa ne idan dattawan suka hadu dan neman shawaran

juna, saboda a karshe abun alheri suke fitarwa. Idan muna so mu ci gaba a Najeriya, ya kamata mu fara yin ĩmãni da Allah, saboda, bai yi ku yi kuskure da ya hallice mu a ‘yan Nijeriya ba. Da Allah ya so da zai iya halittan mu a matsayin yan Asiya, Turawa ko Amirkawa, amma ya zabe mu matsayin a ‘yan Nijeriya.

Bana ganin wa’yanda suka son raba Najeriya a matsayin yan kabila daya, ina ganin su a matsayin yan kungiya mai zaman kanta.

Na kai ziyara wajaje daban-daban a kasannan daga arewa zuwa kudu, na kuma tattauna da kungiyoyin da yakamata dan samun zaman lafiya. Kwanannan na rattaba hanun a takarda zaman lafiya tsakanin Arewa da wasu
kungiyoyi a jihar Owerri.

A nawa fahimatar akwai wasu da suke kashe kudade akan wannan matsalan dan daukaka kansu.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Advertisement