Wasanni

Madrid za ta kara da Man City a Amurka

Real da City za su kece raini a International Champions Cup a Amurka

Kungiyar Real Madrid za ta kara da Manchester City a gasar International Champions Cup a ranar Alhamis a Amurka.

 

Wannan ne karo na biyu da kungiyoyin za su kara a gasar ta International Champions, kuma a wasan farko da suka yi a Australia kaka biyu da ta wuce, Real ce ta doke City 4-1.

Cikin haduwa hudu da aka yi tsakanin kungiyoyin biyu, Real Madrid ta ci wasa biyu sannan suka yi kunnen doki a karawa biyu.

A gasar bana Manchester City ta yi rashin nasara a hannun Manchester United da ci 2-0, sannan United ta yi nasara a kan Madrid a bugun fenariti, bayan da suka tashi kunnen doki 1-1.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.