Wasanni

Lukakau na son kafa tarihi a Man United

Romelu Lukaku ya ce yana kafa sabon tarihi na kashin kansa a Manchester United.

Dan kwallon na kasar Belgium mai shekara 24, ya koma United ne kan kudi fan miliyan 75 bayan ya zura kwallo 25 a gasar Firimiya a Everton a kakar da ta gabata.

 

Lukaku, wanda shi ne dan wasan kasar waje na farko da ya zura kwallo 80 a Firimiya kafin ya cika shekara 24, ya ce: “ba zan iya cewa burina ya cika ba tukunna.

“Akwai sauran aiki a gabanmu, kuma in farin ciki da hakan, domin yana nufin cewa zan kara gogewa fiye da yadda na ke.”

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.