Siyasa

Ina Nan Daram A Jam’iyyar APC, Cewar Kwankwaso

Yau kuma zargi gwamnatin Kano da daukar nauyin masu yada jita-jitar komawarsa PDP

Daga Aliyu Ahmad

Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya karyata jita-jitar dake yaduwa cewa da shi da wasu ‘yan majalisu sun sauya sheka daga APC zuwa PDP.

 

Da yake magana da majiyarmu ta ‘Daily Nigerian’ a safiyar yau Talata, shugaban ma’aikatan Sanatan, Aminu Abdulsalam, ya ce babu kanshin gaskiya a labarin kuma labari ne mara tushe.

Kamar yadda ya ce Sanata Kwankwaso da shi da magoya bayansa ba su da niyyar sauya sheka zuwa wata jam’iyyar a ko yaushe.

Ya ce gwamnatin Kano ce ta dauki nauyin yada jita-jitar saboda sun ga uwar jam’iyyar APC ta kasa ta tabbatar da Umar Doguwa a matsayin shugaban jam’iyyar APC na Kano.

Aminu Abdulsalam ya ce wannan ba shine karo na farko da gwamnatin Kano take daukar nauyin yada irin wadannan jita-jitar ba don ganin ta batawa Sanatan suna.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Advertisement