Kannywood

Ina Masoya Hadiza Gabon za ta je Amurka

SHIN WANE FARIN CIKI KUKE JI KO BAKIN CIKI RUBUTA RA AYINKA A KASA

 
Hadiza Gabon da Hauwa Maina sun dade su na fitowa a fina-finan Hausa a Najeriya da ake kira Kannywood.

Fitacciyar ‘yar wasan Kannywood, Hadiza Gabon da wasu masu shiryawa da ba da umarni a fina-finan Hausa za su je Amurka.

‘Yan Kannywood din za su halarci wani taron karawa-juna-sani na mako biyu ne, a wata makarantar koyar da dabarun shirin fim da ke katafaren cibiyar shirin fim ta LA Studios Center.

A ranar Talata 9 ga watan Fabarairu ne jaruman za su tashi zuwa Amurkan. 

Sauran jaruman da za a yi tafiyar da su, su ne: Ali Nuhu da Hauwa Maina.

A cikin masu shiryawa da bayar da umarni kuwa, da akwai Hafizu Bello da Kamal Sani Alkali, da Nazifi Asnanic da Bello Mohammed Bello, da kuma Hassan Giggs.

A yayin ziyarar, za su ga yadda ake shirya fim na zamani, za kuma su koyi sababbin dabaru na shirin fim wanda zai taimaka wa fina-finan Hausa da aka fi sani da Kannywood.

A hirar da BBC ta yi da Mohammed Sani, na kamfanin da ya shirya tafiyar ya ce, ziyarar hadin gwiwa ce da wani kamfani mai son taimakawa shirin fina-finai a Najeriya, musammnan wadanda ake yi da Hausa, saboda tasirinsu da kuma karbuwarsu a duniya.

Wannan ziyara ta zo ne a lokacin da ake shirin bikin bayar da kyatuttuka na Kannywood Awards a watan Maris, da kuma bikin cika shekaru 25 da soma fina-finan Hausa a Najeriya.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.