Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Daukar ‘Yan Sanda Dubu 10 Kowacce Shekara

A yunkurin ta na kawo karshen karancin jami’an tsaro da ake fuskanta a kasar, gwamnatin tarayya ta baiwa rundunar ‘yansanda damar daukar sabbin jami’ai har guda 10,000 a duk shekara.
Babban Sifeton ‘yan sanda, Ibrahim Idris shi ya tabbatar da haka yayin da ya ke jagorantar wani taro na manyan jami’an ‘yan sanda a birnin tarayya Abuja.
Idris ya ce wannan mataki ya zama wajibi idan har za a kawo karshen aikata miyagun laifuka a Nijeriya.
Ya ce a yanzu haka akwai dan sanda daya ga kowanne mutum 400 a Nijeriya, kuma wannan mataki zai taimaka wajen rage wannan alkaluma.
Babban sifeton ‘yan sandan ya kuma yi kira ga majalisa da ta gaggauta sanya hannu a kan kudirin da aka gabatar mata na kara adadin kudaden da ake warewa hukumar ‘yan sandan kasar.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.