Labarai

Gwamnatin Kaduna Za Ta Shirya Gangamin Murnar Dawowar Buhari

Gwamnatin jihar Kaduna karkashin jagorancin Malam Nasir El-Rufa’i, Tana Gayyatar Yan Nijeriya, musamman mazauna jihar, zuwa wajen Gangamin Taron Murnar dawowar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, da kuma kara jaddada goyon baya ga Gwamnatinsa.

Ana Gayyatar dukkanin Kungiyoyi dama dai-daikun mutane.

 

Kuma Ana kira ga dukkan Kungiyoyi da su taho da Banner wacce take dauke da sunan kungiyar tasu da kuma yankin da suka fito.

Za’a gudanar da wannan taro kamar haka:
Rana: Talata 22 ga watan Augusta, 2017.
Lokaci: 9:30 na safe.

Wuri: Murtala Square, Kaduna.

Allah yabada ikon zuwa. Ameen

Sanarwa daga Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, da kuma Mai bawa Gwamnan Shawara akan harkokin Siyasa, Malam Uba Sani.

 

Source In Jaridar Rariya

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.