Labarai

An ceto ‘yan makaranta shida da aka sace a Lagos

Satar mutane domin karbar kudin fansa ta zama ruwan dare a Najeriya

Hukumomi a birnin Lagos da ke kudancin Najeriya sun ce sun ceto ‘yan makarantar da aka sace a birnin.

A watan Mayu ne dai wasu ‘yan bindiga suka sace ‘yan makaranta guda shida.

 

‘Yan bindigan sun kai hari ne a makarantar Igbonla Model School, inda suka tafi da dalibai guda 10.

Amma rahotanni sun ce sun saki hudu daga cikinsu, bayan da suka binciki asalin iyayensu.

‘Yan sanda sun ce ‘yan bindigar sun samu shiga makarantar ta cikin wani daji da ke gefen makarantar ne, inda suka yanka wayar da ta zagaye makarantar kana suka shiga ciki.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.