Labarai

BUKIN SALLAH: Ba za mu daga jarabawar 4 ga watan Satumba ba – WAEC

Hukumar shirya jarabawar kammala sakandare na kasashen yammacin Afrika WAEC ta ce ba za ta daga jarabawar da za a yin a ranar 4 ga watan Satumba ba duk da cewa ranar hutun Eid-el-Kabir ne a Najeriya.

Jami’in da ke kula da harka da jama’a na hukumar Demianus Ojijeogu ya sanar da haka a ranar Laraba da yake hira da gidan jaridar PREMIUM TIMES.

Ya ce hukumar ba za ta daga jarabawar 4 ga watan Satumba ba saboda hutun.

Gwamnatin tarayya ta ba da hutu ranar 1 da 4 ga watan Satumba.

 

Source PMHausa

About the author

Haarun

Co-founder Arewablog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Advertisement