Labarai

Boko Haram: An rasa rayuka 4 – NEMA

Hukumar Agajin Gaggawa ta Kasa, NEMA, ta tabbatar da cewa Boko Haram sun kai hari a sansanonin gudun hijira biyu, har sun kashe mutane hudu.

A cikin wani bayani rubutacce da suka raba wa manema labarai, hukumar ta ce ‘yan gudun hijira hudu sun rasa ran su sannan kuma wasu 15 sun samu raunuka.

Hare-haren dai an kai su ne a sannsani a daya da kuma na biyu da ke Maiduguri.
Sanarwar ta ce :’’A nan take mutane biyu suka mutu, yayin da sauran biyu kuma su ka mutu a asaibiti.”

“An ga gilmawar wata yarinya ‘yar-kunar-bakin-wake a lokacin da ta ke tsallaka shingen waya. Anan take aka harbe ta, yayin da nakiyar da ke daure a jikin ta ta fashe kuma ta dagargaza naman jikin ta.”

Bayanin ya kara da cewa an kuma harbe wata ‘yar-kunar-bakin-wake a Kofar shiga Jami’ar Maiduguri.

About the author

Haarun

Co-founder Arewablog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.