Labarai

Boko Haram: An kashe ma’aikatan jami’ar Maiduguri biyar

An ba wa rundunar sojin Najeriya wa’adin kwana 40 da su kamo shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau

Wasu ma’aikatan Jami’ar Maiduguri guda biyar sun mutu yayin da sojojin kasar ke kokarin kwato su daga hannun kungiyar Boko Haram, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

 

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i a Najeriya (ASUU) reshen Jami’ar Maiduguri, Dokta Dani Mamman, ya ce ma’aikatan jami’ar biyar ne suka rasu cikin ma’aikata tara da suka je aikin binciken danyen mai a yankin Tafkin Chadi.

Tun daga farko dai rundunar sojin Najeriya ta fitar da sanarwar cewa ta ceto wasu daga cikin ma’aikatan da Boko Haram ta kama a lokacin da suka je binciken danayen mai a yankin.

A sanarwar da kakakin rundunar, Sani Usman Kukasheka, ya fitar rundunar sojin Najeriya dai ta ce sojoji tara ne suka rasu a lokacin da suke neman kwato malaman daga hannun kungiyar Boko Haram.

A hirarsa da abokin aikinmu, Aliyu Tanko, Dokta Mamman ya ce mutanen jami’ar na fatan za a samo sauran ma’aikatan jami’ar hudu da rai yayin da yake jajantawa sojin kasar game da rasa dakarunta da ta yi.