Labarai

Bayan an tara masa miliyan N200, Davido ya bada tallafin miliyan 250 ga gidajen marayu

Fitaccen mawaƙin Nijeriya ɗin nan, David Adeleke, ya sanar da tallafin naira na gugar naira har miliyan 250 ga gidajen marayu na ƙasar nan.

Kwanaki biyu da su ka gabata ne a ka tarawa Davido kimanin naira miliyan 2000 bayan da ya nemi a tara masa ya ɗauki motarsa.

Ai kuwa a yau Asabar sai ga Davido ɗin ya sanar a wata sanarwar da ya fitar cewa ya bada tallafin miliyan 250 domin taimakawa marayu a ƙasar nan.

Da ma mawaƙin ya baiyana cewa zai bada tallafin kuɗaɗen da a ka haɗa masa ga marasa ƙarfi.

Ya kuma baiyana cewa ya kafa kwamiti don tantance gidajen marayun da za su ci gajiyar kudin a fadin kasar nan.

Tags

About the author

Haarun

Co-founder Arewablog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.