A wata tattaunawa da kafafen yada labarai da tayi a baya, Aisha Wakili ta tabbatar da cewar Shugaban Boko Haram na farko Muhammad Yusuf da Mataimakin Shi Abubakar Shekau, babu inda suke hira a garin Maiduguri sai a gidan ta, su kan ci abinci su yini suna hira a gidanta.
Aisha Wakili wacce asalin ta Inyamura ce daga kudancin Nijeriya, ta karbi addinin Musulunci ne lokacin da take karatun aikin Lauya a Jami’ar Maiduguri, inda ta zabi sunan Aisha a matsayin sabon sunan ta na Musulunci, kuma ta auri Barista Muhammad Wakili Ghana, ma’aikaci a Kotun daukaka kara da ke Maiduguri.
Aisha Wakili ta bayyana ‘ya’yan Boko Haram a matsayin mutane masu saukin kai da ladabi, domin ita kanta suna kiran ta da suna Mama, sai dai kuma suna da tsanani a wajen kishin Addinin Musulunci, sannan suna adawa da sunan da aka kakaba musu na Boko Haram, domin halastaccen sunan su shine Jama’atu Ahalus Sunnah Lil Da’awati Wal Jihad.
A shekarar 2016 Rundunar Sojojin Nijeriya Karkashin Jagorancin Janar Tukur Yusuf Buratai ta gayyaci Aisha Wakili domin amsa wasu tambayoyi dangane da harkokin Boko Haram.
Barista Aisha Wakili, Mama Ga 'Yan Boko Haram

Add Comment