Kannywood

Ban auri Sadiya Gyale ba— Baballe

Fittaccen jarumin fina-finan Hausa, Baballe Hayatu, ya musanta rahotannin da ake yada wa cewa an daura aurensa da Sadiya Gyale.

A hirar da ya yi da BBC, Baballe ya ce wani abokin aikinsa ne a Kannywood ya kirkiri labarin, ya kuma sa shi a shafukan sada zumunta da muharawa wanda kuma ya yadu kamar wutar daji.
Jarumin ya ci gaba da cewa sakamakon wannan labari har Ali Nuhu ya yi fushi da shi ganin cewa suna tare amma bai sanar da shi daurin auren ba.
Ya kuma kara da cewa Sadiya ta tafi umara a Saudiyya ba ta kuma san da labarin ba, ya kuma ce babu maganar aure a tsakaninsu sai dai mutunci.

About the author

Mr. ArewaBlog

C.E.O/Founder ArewaBlog

Add Comment

Click here to post a comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.