Labarai

An Ceto Jami’an Ofishin Jakadancin Amurka Da Aka Sace A Najeriya

An Ceto Jami’an Ofishin Jakadancin Amurka Da Aka Sace A Najeriya

 

Rundunar ƴan sandan Najeriya a jihar Anambra ta ce ta samu nasarar ceto mutum biyu waɗanda aka sace a harin da aka kai kan tawagar ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka a Najeriya, a jihar Anambra.

Katsina Reporters

A wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, mai magana da yawun rundunar ƴan sanda a jihar, Ikenga Tochukwu ya ce an ceto mutanen biyu ba tare da wata jikkata ba.

 

Sai dai bai bayyana sunayen waɗanda aka ceto ɗin ba.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa jami’an tsaro na ci gaba da bincike kan lamarin domin samun cikakken bayani.

 

A ranar Talata ne wasu ƴan bindiga suka yi wa kwambar motocin da ke ɗauke da ma’aikatan kwantar-ɓauna, inda suka kashe mutum bakwai, ciki har da ma’aikata uku.

 

Maharan sun kuma tafi da wasu daga cikin ma’aikatan sannan suka ƙona motocin.